Jam’iyar adawar Faransa ta UMP ta dauki matakin dinke barakarta
Wallafawa ranar:
Jama’iyyar adawa ta UMP a Faransa, ta dauki matakin dinke barakar da ta kunno kai tsakanin ‘Ya ‘yan ta, lamarin da ya kawo rarrabuwan kanun shugabannin jama’iyyar.
Yanzu shugabannin da ke adawa da juna sun yarda a sake sabon zaben shugabancin jama’iyyar, a watan satumban shekara mai zuwa, don warware matsalar.
Bayan shafe wata guda ana takun saka , Jean-Francois Cope, da ya lashe zaben shugabancin jama’iyyar, da aka yi a watan da ya wuce, ya amince a sake zaben bayan tattaunawa ta wayar tarho da abokin hamayyar shi, tsohon Firaminista, Francois Fillon.
A baya Cope ya ki amincewa da duk wani zaben da za a shirya kafin zaben kasar na shekarar 2014.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu