Faransa

An kai hari a Ofishin asusun bayar da lamuni a Paris

Ofishin asusun bayar da Lamuni na IMF da ke Paris na kasar Faransa
Ofishin asusun bayar da Lamuni na IMF da ke Paris na kasar Faransa 路透社REUTERS/Christian Hartmann

Mutum daya ya samu rauni sakamakon fashewar wani abu da aka kunshe a wasika da aka tura wa babbar cibiyar Asusun bayar da Lamuni ta Duniya IMF da ke birnin Paris na Faransa a yau alhamis.Bayan fashewar dai ne , jami’an tsaro suka bukaci jama’a su fice daga cikin ginin domin gudanar da bincike. 

Talla

Hukumomin kasar sun sanar da tura yan Sanda  a unguwar domin  karfafa tsaro dama maida hankali wajen gudanar da bicinke a kai.

Da jimawa hukumomin na Faransa suka sanar da daukar matakan da suka dace na tsaro a birane kamar su Paris dama wajejen shakatawa.

Ya zuwa yanzu  ana ci gaba da gudanar da bicinke domin tanttance ainayin abinda ya faru a ofishin asusun bayar da lamuni dake Paris.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI