Jamus

'Dan Bindiga Ya Kashe Mutane Biyu A Gidan Rawa Na Kasar Jamus

Shugaban Gwamnatin Jamus  Angela Merkel
Shugaban Gwamnatin Jamus Angela Merkel RFI

A kasar Jamus mutane biyu sun gamu da ajalinsu a wani gidan rawa, wasu mutanen hudu kuma suka jikkata sakamakon hare-harbe a wani gidan rawa kafin wayewar gari yau lahadi.

Talla

Wata sanarwa daga ‘yan sandan kasar na cewa wani mutun mai kimanin shekaru 34 ya aikata harbe-harben.

Sanarwar ‘yan sandan na cewa an jikkata maharin a lokacin da ‘yan sanda ke kokarin kama shi yana shirin tserewa don barin  gidan rawan amma kuma daga bisani ya mutu a asibiti.

Wannan hari na zuwa ne kwanaki biyu bayan wani harin da wani mutun dauke da wuka ya kai shagon saida kayayyaki inda aka sami hasarar rayuka a garin Hamburg.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI