Faransa

Kotun Faransa ta umarci bude kayan tarihin Mitterand don binciken kisan Rwanda

Babbar Kotun mulkin Faransa ta bada umurnin bude kayayyakin tarihin tsohon shugaban kasa Francois Mitterand domin baiwa wani mai bincike damar duba takardun da ke da nasaba da kisan kiyashin da akayi a kasar Rwanda a shekarar 1994.

Tsohon shugaban kasar Faransa, Francois mitterand.
Tsohon shugaban kasar Faransa, Francois mitterand. GEORGES GOBET / AFP
Talla

Kotun ta ce umurnin zai baiwa mai binciken Francois Graner damar nazarin bayanan asiri da za suyi karin haske kan kisan wanda jama’a ke so suji.

Zarge zarge da dama sun biyo bayan kisan kare dangin na Rwanda da kuma rawar da gwamnatin Faransa ta taka lokacin, abinda ya haifar da takaddama tsakanin kasashen biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI