Faransa

Asibitocin Paris sun tumbatsa da masu corona

Hukumomin Faransa sun ce asibitocin birnin Paris na gaf da cika, ganin yadda marasa lafiyar da ke fama da cutar coronavirus suka mamaye kashi 90 na gadajen  da ake da su.

Cutar coronavirus ta sake barkewa karo na biyu a kasashen Turai.
Cutar coronavirus ta sake barkewa karo na biyu a kasashen Turai. AFP / MICHAEL DANTAS
Talla

Shugaban Hukumar Kula da Asibitocin birnin  ya bukaci a  kara zage dantse dangane da shirin tarbar wata sabuwar ambaliyar masu fama da annobar wadda ta sake kunno kai a karo na biyu.

Mista Martin Hirsch da ke shugabntar asibitoci 39 na birnin Paris ya ce ba za a iya kauce wa faruwar ambaliyar mutanen da suka kamu da cutar ta Covid 19 ba a kasar musaman a birnin Paris.

A cikin sa'o'i 24 da suka gabata, an gano akalla mutane 800 zuwa dubu 1 da suka kamu da cutar ta Covid 19, alkalumman da ke nuna cewa, an samu karin marasa lafiyar da kimanin kashi 70 zuwa 90 cikin 100 a birnin na Paris kadai.

Wannan dai ya kara jefa shugaba Emmanuel Macron cikin halin tsaka mai wuya, yayin da ake sa ran zai bayyana ga al’ummar kasar a wata tattaunawa ta talabijin da za a watsa a maraicen wannan Larabar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI