Adadin mutanen da girgizar kasa ta kashe a Turkiya ya kai 100
Adadin mutanen da suka mutu a girgizar kasar Turkiya ya karu zuwa mutum 100 yau Talata inda ake da jumullar mutum 994 da suka jikkata a ibtila’in.
Wallafawa ranar:
Sanarwar da hukumar kula bal’o’i ta Turkiya ta fitar ta ce girgizar kasar mai karfin maki 7 da ta dirarwa kasar cikin makwan jiya ta yi mummunar barna inda kawo yanzu ake ci gaba da laluben wadanda suka bace a baraguzan gine-gine.
Acewar hukumar yanzu haka akwai jumullar mutum 147 da ke karbar kulawa a Asibitoci yayinda ake ci gaba da zakulo wasu da sauran ransu a karkashin gine-ginen da suka zube.
Yanzuy haka dai a yankin Izmir da ibti la’in ya fi tsananta ana ci gaba da aikin ceto bayan nasarar zakulo yarinya mai shekaru 3 da ranta duk da shafe kwanaki 3 a karkashin gine-gine ko da ya ke dan uwanta da ginin ya bunne su tare ya rasa ransa lokaci kankani bayan fito dashi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu