A wannan shirin na labarin, za mu duba shan kaye da ‘yan kasashen Nigeria da na africa ta kudu, wato Ibrahim Galadima da Danny Jordaan, da suka fito takara don wakiltar nahiya Africa a kwamtin gudanarwan hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, inda kuma suka sha kasa a zaben, inda Jacques Anouma na kasar Cote d’Ivoire da Mohamed Rouaroua na Algeria suka dare kujerun da za su wakilci nahiyar ta Africa, mutane da dama suna ganin shan kashin na dan Nigeria Ibrahim Galadima, bai rasa nasaba da lamarin nan na abin kunya kan zargin yunkurin karban na goro don zaben kasar da za ta dau nauyin wasannin kwallon kafa na duniya, da ake wa dan Nigeria nan Mr Amos Adamu.Za kuma mu leka filin kwallon dawaki wato polo, don a makon daya wuce ne aka fara wasan kwallon dawaki na shekarar 2011 a garin Lagos. Mutane da dama suna cewa wasan kwallon dawaki, wasa ne mai ban sha’awa da ake yi a kan doki, to amma sai dai a lokuta da dama in ana wannan wasan, ba kasafai za ka ga mutane sun je don kashe kwarkwatar idanun su ba, ko me ya sa? Za dai mu duba wannan a cikin shirin na yau. Wanda ni nasiruddeen Muhammad zan gabatar
Sauran kashi-kashi
-
Wasanni 'Yan wasa bakaken fata na fuskantar wariya a Turai Shirin na wannan lokaci ya mayar da hankali ne, akan batun nuna wariyar launin fata da ‘yan wasa bakar fata ke fuskanta a nahiyar Turai.29/05/2023 09:55
-
Wasanni Bahaushiya Mace ta farko da ke horar da 'yan wasan kwallon kafa Maza Shirin Duniyar wasanni tare da Khamis Saleh a wannan mako ya leka garin Mai Tsidau ne a Karamar hukumar Makodan Jihar Kano ta arewacin Najeriya, dan kawo muku yadda wata baiwar Allah mai suna Coach Fatima, wadda ta zamo mace daya tilo da ke horas da kungiyar kwallon kafa ta maza, wadda zancen nan da ake tuni labarinta ya karade kafafen sada zumunta a Najeriya.15/05/2023 09:59
-
Wasanni Halin da tsoffin 'yan wasan kwallon kafar Najeriya ke ciki Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan mako tare da Khamis Saleh ya maida hankali ne kan halin kunci da wasu tsoffin 'yan wasan kwallon kafar Super Eagles ta Najeriya da suka wakilci kasar a matakai daban-daban ke ciki.24/04/2023 10:00
-
Wasanni Duniyar Wasanni: Tarihin Mesut Ozil tsohon dan wasan Jamus Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan mako tare da Khamis Saleh ya duba tarihin tsohon dan wasan tawagar kasar Jamus da ya yi murabus daga buga kwallon kafa a ‘yan kwanakin nan wato Mesut Ozil.10/04/2023 09:58
-
Wasanni Yadda ake ci gaba da fafata gasar Super League din kasar Niger Shirin "Duniyar Wassani" na wannan makon ya leka ne Jamhuriyar Nijar inda ake ci gaba da fafatawa a gasar lik din kasar.An kammala wasan zagaye na farko a gasar lik din Jamhuriyar Niger, da kungiyoyi 14 ke fafatawa a cikin ta.Gasar ta bana ta fuskanci tsaiko da dama ganin yadda a tsakayar ta aka tafi hutu don halartar gasar CHAN, sannan kuma aka sake bada hutu ga 'yan wasa bayan kammala gasar.13/03/2023 09:57