Kwallon kafa

Zakarun Turai: Chelsea da Benfica, APOEL zata nemi ba Madrid mamaki

'Yan wasan Bayern Munich  Arjen Robben da Ivica Olic da Danjel Pranjic  a lokacin da zasu hau jirgi zuwa kasar Faransa domin karawa da kungiyar  Marseille a gasar Zakarun Turai.
'Yan wasan Bayern Munich Arjen Robben da Ivica Olic da Danjel Pranjic a lokacin da zasu hau jirgi zuwa kasar Faransa domin karawa da kungiyar Marseille a gasar Zakarun Turai. REUTERS/Michael Dalder

A Gasar Zakarun Turai, Kungiyar APOEL ta kasar Cyprus zata fafata da Real Madrid inda wasu suke ganin Madrid ta samu garabasa a wasan Quarter Final amma dubban masoya APOEL ne suka saye tikitin shiga kallon wasan domin fatar ba Real Madrid mamaki.

Talla

A daya bangaren kuma Chelsea zata kara ne da Benfica, kuma Kocin Chelsea Roberto Di Matteo tsohon dan wasan Benfica ne, kuma akwai tsoffin ‘yan wasan Benfica a tawagar Chelsea wato Ramires da David Luiz wadanda suka taka kwallo a Benfica kafin zuwansu Chelsea.

A karshen mako, Chelsea bata sha dadi ba hannun Tottenham a Premier domin an tashi wasan babu ci.

Tsakanin Chelsea da Benfica cikin duk kungiyar da ta tsallake ita ce zata hadu da Barcelona ko AC Milan a wasan kusa da karshe.

A bana dai babu hamayya tsakanin Barcelona da Real Madrid domin ba zasu iya haduwa ba sai a wasan karshe da za’a gudanar a ranar 19 ga watan Mayu.

Wannan ne karo na farko da wata kungiya daga Cyprus ta tsallake zuwa zagayen Quarter final a gasar zakarun Turai.

A gobe Laraba ne dai AC Milan zata karbi bakuncin Barcelona a San Siro.

Bayern Munich kuma zata kai ziyara Faransa domin fafatawa da Marseille.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI