Wasan Dambe

Za a fara horar da matasa a fagen wasan damben Ghana

Wata kungiya mai zamankanta, a kasar Ghana, ta shirya wata horarwa ga matasa masu sha’awan damben zamani, a irin kokarinta na ganin cewa ta farfado da wasan dambe a kasar. A cewar shugaban kungiyar, Atta Lartey, horarwar za ta hada matasa wadanda ke tsakanin shekaru 12 ne zuwa 16. 

Tsohon dan wasan duniyan dambe, kuma dan kasar Ghana, Joseph Agbeko "King Kong"
Tsohon dan wasan duniyan dambe, kuma dan kasar Ghana, Joseph Agbeko "King Kong" www.law.com
Talla

Ya kara da cewa a irin wannan horarwarce aka lalubo shahararren dan wasan damben duniya, Joseph Agbeko, wanda aka fi sani da King Kong, wanda kuma dan kasar Ghana ne.

A cewar kungiyar, gudanar da horarwar zai taimaka wajen maye gurbin da tsofaffin ‘Yan dambe na kasar su ka bari, kuma ya lalubo sabbin ‘Yan wasan.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI