CAF
Hukumar CAF za ta zabi gwarzon Afrika
Wallafawa ranar:
Hukumar CAF da ke kula da kwallon kafa a Nahiyar za ta zabi gwarzon dan wasan Afrika tsakanin ‘Yan wasan Cote d’voire guda biyu Didier Drgba da Yaya Toure da kuma dan wasan Kamaru Alexendre Song.
Talla
Drogba dai shi ne ya taimakawa Chelsea lashe kofin zakarun Turai karo na farko yayin da kuma Yaya Toure mai rike da kambun ya lashe kofin Premier a Manchester City.
Wannan ne kuma karon farko da hukumar CAF ta zabi Alex Song domin ba shi kyautar bisa irin rawar da ya taka a Arsenal kafin ya koma taka kwallo a Barcelona.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu