Wasanni

Liecester da Juventus sun yi nasarar zuwa matakin gaba a gasar Zakarun Turai

Da wasan Leicester Wes Morgan da mai tsaron gida Kasper Schmeichel na murna
Da wasan Leicester Wes Morgan da mai tsaron gida Kasper Schmeichel na murna Reuters

Leicester City ta yi nasasar zuwa zagayen da ke biye wa na kusa da na karshe wato Quater-finals a gasar neman kofin Zakarun Turai, bayan da ta doke Sevilla a karawar da suka yi cikin daren talata a matsayin ci 2-1.

Talla

Juventus kuwa ta yi nasarar wucewa zuwa wannan mataki ne bayan da ta doke Porto.

Wannan dai na nufin cewa Juventus da Liecester sun shiga sahun kungiyoyin da za su kara a zagayen Quarter-finals da suka hada da Barcelona, Bayern Munich, Borussia Dortmund da Real Madrid.

A ranar juma’a mai zuwa za a fitar da jadawali da ke fayyace kungiyoyin za su kara da juna.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI