Wasanni

An koma fagen-daga a gasar firimiyar Ingila

Yau ake komawa gasar firimiyar Ingila bayan kwashe kwanaki 100 da dakatar da ita sakamakon annobar coronavirus, inda a yau din za a fafata tsakanin Manchester City da Arsenal.

Kwanaki 100 raban da aka taka leda a gasar firimiyar Ingila
Kwanaki 100 raban da aka taka leda a gasar firimiyar Ingila Reuters
Talla

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya ce, har yanzu ‘yan wasansa ba su kintsa wa wannan karawar ba duk da cewa, babu wanda aka rawaitio yana fama da rauni a cikinsu.

Za a yi wasan ne ba tare da ‘yan kallo ba ko kuma magoya baya saboda matakan da aka ci gaba da aiwatar da su na hana yaduwar cutar coronavirus a Birtaniya.

Sai dai masoya kwallon kafa a sassan duniya za su samu damar kallon wasan ta kafafen talabijin.

To a bangare guda, Liverpool na fatan lashe kofin firimiyar Ingila a karon farko cikin shekaru 30, kuma muddin Manchester City ta yi rashin nasara a hannun Arsenal a , to babu shakka, Liverpool karkashin jagorancin kocinta Jurgen Kloop, za ta dage wannan kofin a ranar Lahadi da take fatar casa Everton.

Liverpool ce ke jan ragama a teburin firimiyar Ingila da banbancin maki 25.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI