Babu siddabarun da zai ceto Arsenal sai ta sayi manyan 'yan wasa-Arteta
Kocin Arsenal Mikel Arteta ya ce babu wani siddabaru da zai iya aiwatarwa don yin takara da kungiyar kwallon kafa ta Liverpool a kaka mai zuwa idan har mahunkuntar kungiyar ba su fidda kudi sun sayi manyan ‘yan wasa ba.
Wallafawa ranar:
Arteta ya yi wannan bayanin ne bayan da tawagarsa ta doke zakarun gasar Firimiyar Ingilar da ci 2 da 1 a daren jiya Laraba.
Duk da cewa Liverpool ta yi rashin nasara a hannun Arsenal wanda shine rashin nasararta karo na 3 a wannan kaka, Liverpool ta baiwa Arsenal, wacce ke a matsayi na 9 tazarar maki 40.
Arsenal na kan hanyar kammala gasar Firimiyar Ingila a matsayi mafi kaskanci da ta tsinci kanta tun a kakar wasa ta 1994/95.
Arteta ya tada kafadar wannan tawaga ta ‘yan wasan Arsenal tun da ya kama aikin horar da ita a watan Disamba, kuma ya ce ya yi na’am da irin kwazon ‘yan wasansa.
Sai dai abu ne mai kamar wuya a baiwa Arteta kudade masu yawa don sayen ‘yan wasa a kaka mai zuwa duba da cewa ba za a dama da kungiyar a gasar zakarun nahiyar Turai a kaka mai zuwa ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu