Wasanni

Najeriya ta karrama 'yan wasa 60 saboda cika shekaru 60

Wallafawa ranar:

Shirin Duniyar Wasanni tare da Abdurrahman Gambo Ahmad ya yada zango ne a birnin Abuja na Najeriya, inda aka gudanar da gagarumin bikin karrama tsoffin 'yan wasan da suka kwashe tsawon rayuwar kuruciyarsu wajen hidimta wa kasar tare da daga martabarta a idon duniya. Gwamnati ta bada kyautukan ne ga tsoffin 'yan wasa 60 a daidai lokacin da ta cika shekaru 60 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka na Birtaniya.

Ministan Wasanni da Matasa na Najeriya Sunday Dare
Ministan Wasanni da Matasa na Najeriya Sunday Dare Daily Trsut