Liverpool da Borussia Dortmund sun fice daga gasar zakarun Turai
Wallafawa ranar:
Kungiyoyin kwallon kafa na Man City da Real Madrid sun bi sahun takwarorinsu na Chelsea da PSG wajen samun gurbi a wasannin gab da na karshe na cin kofin zakarun Turai yayin da suka yi waje da kungiyoyin Liverpool da Borussia Dortmond a karawar da ta gudana daren jiya.
Real Madrid ta yi nasarar fitar da Liverpool ba tare da zura kwallo ko guda daga bangaren kungiyoyin biyu a karawar ta jiya ba, amma da ya ke tana da rinjayen kwallaye 3 da 1 da ta zurawa tawagar ta Ingila a haduwar farko hakan ya bata damar tsallakawa mataki na gaba.
A bangare guda ita kuma City ta yi nasarar zurawa Dortmund kwallaye 2 da 1 wato kwatankwacin yadda suka tashi a haduwar farko wanda ya bata fifikon maki akanta.
Tun farko Borussia Dortmund ce ta fara zura kwallo a karawar ta hannun dan wasanta Bellingham a minti na 39 da fara wasa kafin tafiya hutun rabin lokaci amma kuma City ta farke bayan samun bugun fenariti kana ta kara kwallo ta biyu a minti na 75.
Yanzu haka Real Madrid za ta hadu da Chelsea ne yayinda Manchester City za ta hadu da PSG a zagayen gab da na karshe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu