Macron zai ci gaba da goyan bayan dakarun Faransa
Daruruwan mutane ne suka yi gangami a birnin Paris domin karrama sojojin kasar 13 da suka mutu sakamakon hadarin jiragen sama a Mali, lokacin da suke yaki da yan ta’adda.Shugaba Emmanuel Macron da takwaran sa na Mali, Ibrahim Boubacar Keita suka jagoranci bikin.
Wallafawa ranar:
Shugaban Faransa ya bayyana alhinin sa tareda daukar alkawali na dafawa dakarun kasar a yakin da suke yi da yan ta'adda a Mali.
Faransa na daya daga cikin manyan kasashe dake taka gaggarumar rawa a yakin da take yi da yan ta'adda a yankin Sahel.
Shugaban Mali Ibrahim Boubacar Keita da ya halarci wadanan addu'o'i ya jajintawa iyalan sojojin da suka rasa rayukan su a fagen yaki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu